in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Najeriya ya lashi takobin karbo dukiyar kasa daga hannun tsoffin shugabanni
2015-08-18 13:31:15 cri
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya lashi takobin karbo dukiyar kasa da har yanzu take a hannun tsoffin shugabannin kasar, in ji fadar shugaban kasa a ranar Litinin.

Kakakin shugaban Najeriya, Garba Shehu, ya bayyana ma manema labarai cewa kwamitin da aka dora wa nauyin wannan aiki na karbo dukiyar kasa da ke hannun tsoffin shugabannin siyasa na kasar zai fara aiki ba da jimawa ba.

Wannan mataki da shugaba Buhari ya dauka na cikin tsarin manufar karbo dukkan dukiyar kasa da aka sace a Najeriya, kasar da ta fi yawan al'umma a Afrika, da kuma kamfen gama gari na yaki da cin hanci, in ji mista Shehu.

Duk da haka, kamfen yaki da cin hanci da rashawa na shugaba Buhari da kuma matakinsa na rage cin hanci sosai a Najeriya na iyar fuskantar tirjiya daga wasu mutanen kasar a matsayin wani bi ta da kulli, maimakon wani aikin da zai taimaka wa kasar.

A cewar wani mai fashin bakin siyasa, Yinka Fayomade, kamfen shugaban Najeriya na yaki da cin hanci, wasu na daukar sa tamkar wani abin da ya riga ya rasa tagomashi wanda kuma aka juya akalarsa kan manyan masu yi ma shugaba Buhari adawa.

Jam'iyyar APC da ke mulki da kuma babbar jam'iyyar adawa ta PDP sun shiga cikin sabanin ra'ayi kan batun yaki da cikin hanci. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China