in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Babban sakataren MDD ya yi Allah wadai da yawaitar hare hare a arewa maso gabashin Nigeria
2015-08-13 10:49:33 cri
Babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya bayyana takaicin sa game da jerin hare haren bomb a kasuwanni dake yankin arewa maso gabashin Nigeria wanda ya yi sanadiyyar hallaka rayukan mutane kimanin 48.

Mista Ban ya bayyana hakan ne a sakon da ya gabatar ta hannun mai Magana da yawunsa Stephane Dujarric, inda ya ce babu dalilin da zai sa a kashe rayukan mutanen da ba su ji ba ba su gani ba.

A kalla mutane 48 ne suka hallaka a harin bomb na ranar Talatar nan a kasuwar Damboa dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nigeria.

Mista Dujarric ya ce sakataren na MDD ya jaddada aniyar sa na bada dukkanin goyon baya kuma kwamitin MDD a shirye yake ya hada kai da gwamnatin Nigeria domin yakar ayyukan ta'addanci, wanda ya yi dai dai da tsarin dokokin 'yancin dan adam da na 'yan gudun hijira da kuma na jin kai na duniya.

Sai dai har yanzu babu wata kungiya da ta yi ikirarin daukar nauyin wannan harin. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China