in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An amince da shirin da kasashen kudancin Afrika suka fitar na yaki da ta'addanci
2015-08-19 11:34:44 cri

Shugabannin kasashen kudancin Afrika sun amince da shirin yaki da ta'addanci na shiyya-shiyya a yayin taron kungiyar raga kasashen kudancin nahiyar SADC karo na 35.

Shugabannin kasashe da jami'an gwamnatin na kasashen kungiyar ta SADC mai mambobi 15 suka halarci taron shugabannin kasashe da gwamnatoci na shekara shekara tsakanin ranakun Litinin da Talata na wannan makon a Gabarone, babban birnin kasar Botswana.

Sanarwar bayan taron da aka fitar a ranar Talatan ya ce, yankin na bukatar samun manufa da tsari daya ta yadda za'a kare tare da magance duk wassu nau'in ayyukan ta'addanmci daga gida ko kasashen waje.

Kungiyar SADC na daya daga cikin kungiyoyin da kasashen take zaman lafiya a nahiyar.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China