in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata kasashen kungiyar SADC su kara yin hadin gwiwa kan kayayyakin more rayuwa
2014-08-18 11:02:17 cri

A ranar Lahadi 17 ga wata ne aka bude taron koli na kungiyar SADC karo na 34 a wurin shakatawa na Victoria Falls dake kasar Zimbabwe. Taron na kwanaki biyu ya samu halartar shugabannin kasashe membobin kungiyar ta SADC 15 da na kungiyar AU.

A gun taron, Sabon shugaban kungiyar a wannan karo kuma shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe ya jaddada cewa, kamata ya yi kasashe membobin kungiyar su kara yin hadin gwiwa wajen samar da kayayyakin more rayuwa, kana ya yi kira da a gina manyan hanyoyin jiragen kasa a manyan birane da cibiyoyin cinikayya na kasashen don sa kaimi ga samun bunkasuwar masana'antu a nahiyar Afirka.

Taken taron na wannan karo shi ne sa kaimi ga yin amfani da albarkatun da allah ya hore wa yankin da samun bunkasuwa mai dorewa a fannonin tattalin arziki da zamantakewar al'umma, ana fatan gabatar da hadaddiyar sanarwar bayan taro a ranar 18 ga wata. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China