in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bude taron koli na kungiyar SADC karo na 34
2014-08-18 11:01:27 cri

A ranar Lahadi 17 ga wata ne aka bude taron koli na kungiyar SADC karo na 34 a wurin shakatawa na Victoria Falls dake kasar Zimbabwe.

Taron na kwanaki biyu ya samu halartar shugabannin kasashe membobin kungiyar ta SADC 15 da na kungiyar AU. Sabon shugaban kungiyar a wannan karo kuma shugaban kasar Zimbabwe Robert Mugabe ya yi nuni cewa, ya kamata a canja yadda ake sayar da albarkatun kasashen yankin cikin araha, da kuma kara sa kaimi ga yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen dake yankin.

A gun bikin bude taron, Mugabe ya bayyana cewa, allah ya hore wa kasashe membobin kungiyar SADC albarkatun ma'adinai, amma a kan sayar wa kasashen waje cikin araha. Kamata ya yi kasashen yankin su kafa tsarin sha'anin samar da albarkatun ma'adinai, da kuma yin kokarin kara samun sabuwar moriya daga kayayyakin da suka kera da kuma samar da aikin yi ga jama'arsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ga Wasu
v An kira taron koli karo na 33 na kungiyar SADC 2013-08-18 16:45:20
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China