in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 19 sun rasa rayukan su a sabon rikicin kasar Libya
2015-06-11 10:49:32 cri
Wani jami'in ma'aikatar kula da harkokin cikin gidan kasar Libya, ya ce sabon fada ya barke tsakanin dakarun bangarori 2 masu dauke da makamai, a birnin Derna dake yankin gabashin kasar, lamarin da ya haddasa mutuwar a kalla mutane 19.

Jami'in wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya shaidawa wakilinmu cewa, dakarun wata kungiya mai goyon bayan kungiyar Al-Qaeda, da kuma na kungiyar IS ne suka gwabza fada, bisa wani dadadden sabani dake tsakanin su. Jami'in ya kuma kara da cewa, yayin dauki ba dadin, dakaru 3 daga tsagin masu goyon bayan Al-Qaeda sun mutu, yayin da aka harbe mutane 16 daga bangaren kungiyar IS.

Tun dai hambarar da gwamnatin tsohon shugaban kasar ta Libya Muammar Gaddafi a shekarar 2011, ake ta fuskantar matsalolin rashin zaman lafiya, musamman ma daga watan Agustan bara zuwa wannan lokaci, inda majalissu 2 da gwamnatoci 2 ke ikirarin gudanar da mulkin kasar, yayin da kuma magoya bayan kungiyar Al-Qaeda da na kungiyar IS ke ci gaba da samun gindin-zama a kasar. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China