in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana maraba da bangarori daban daban na Libya da su cimma shirin yarjejeniyar siyasa
2015-07-15 13:37:08 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana a yau Labara cewa, kasar Sin tana maraba da yadda bangarori daban daban na kasar Libya suka cimma yarjejeniya a siyasance a tsakaninsu.

Hua ta bayyana haka ne a yayin da take amsa tambayoyin manema labaru game da ra'ayin kasar Sin kan cimma wannan yarjejeniya, inda ta bayyana cewa, kasar Sin tana goyon bayan yunkurin tattaunawar siyasa na Libya karkashin shugabancin MDD, tana kuma maraba da cimma wannan yarjejeniyar siyasa da rukunonin kasar suka yi a kasar Morocco. Ta kuma yi kira ga bangarorin da su ci gaba da sulhuntawa ta hanyar yin shawarwari, da nufin farfado da zaman lafiya a kasar, wannan mataki ya dace da moriyar jama'ar kasar, kana zai taimaka wajen tabbatar da tsaro, zaman lafiya da kuma bunkasuwar yankin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China