in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Afrika na sake dubi cigaban da aka samu kan baiwa mata 'yanci
2015-08-14 11:15:34 cri
Manyan jami'an dake kula da harkokin mata, da kwararru da kuma masu rajin kare hakkin dan adam da suka fito daga kasashe 54 mambobin kungiyar tarayyar Afrika (AU) sun yi wani zaman taro a ranar Alhamis a birnin Nairobi domin nazari kan cigaban da aka samu wajen tabbatar da daidaici tsakanin maza da mata, kamar yadda manyan kudurorin kasa da kasa suka bayyana.

Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya jagoranci bude taron dake neman shata wani sabon yunkuri na baiwa mata da 'yan mata 'yanci tafiyar da harkokin rayuwarsu a kasashen Afrika dake kudu da hamadar Sahara.

Daya daga cikin manyan makasudai na ajandar shekarar 2063 na kungiyar tarayyar Afrika shi ne na aza daidaici jinsuna a matsayin ginshiki na ajandar neman bunkasuwa na nahiyar Afrika. An fi maida hankali kan muhimman fannoni biyar, wato kiwon lafiya, ilimi, tattalin arziki, noma, zaman lafiya da tsaro domin baiwa mata da 'yan mata 'yanci, in ji shugaba Kenyatta. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China