Lamarin ya faru da misalin karfe 5 da mintuna 45 na dare a wani sansanin rukunin sojojin kasar Rwanda. Babu wata masana kan dalilin da ya haddasa wannan kisan kai a halin yanzu. Kuma tuni aka kafa wani kwamitin bincike cikin gaggawa.
Mista Nzabamwita ya kawo maganar ta'addanci, amma kuma ya bayyana cewa akwai yiwuwar matsalar tabin kai.
Sojojin Rwanda dari takwas ne aka jibge a Afrika ta tsakiya tun cikin watan Janairun shekarar 2014, a cikin tawagar wanzar da zaman lafiya ta MDD dake Afrika ta Tsakiya (MINUSAC). (Maman Ada)