in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Uganda ta zamo ta 3 a gasar kwallon kafar tsakiya da gabashin nahiyar Afirka
2015-08-05 09:37:30 cri
Kungiyar kwallon kafar KCCA FC ta kasar Uganda ta zamo a matsayi na 3, a gasar kulaflikan yankin tsakiya da gabashin Afirka ta bana, da aka buga a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzania.

Yayin wasan neman matsayi na 3 a gasar wadda hukumar kwallon kafa ta tsakiya da gabashin Afirka Cecafa, da hadin gwiwar shugaban kasar Rwanda Paul Kagame suka dauki nauyin shiryawa, Uganda ta doke takwararta ta Sudan da ci 2 da 1.

Baya ga lambar tagulla da aka mikawa kungiyar ta kasar Uganda, an kuma baiwa kulaf din kyautar kudi har dalar Amurka 10,000.

Da yake bayyana farin cikin sa game da wannan nasara da kulaf din sa ya samu, mukaddashin babban jami'in kungiyar ta KCCA David Tamale, ya ce hakan babbar nasara ce kasancewar sun hada kungiya mai cike da kwararrun 'yan wasa, da kuma sabbin masu horas da 'yan wasa 2.

A wasan karshe da aka buga a karshen makon jiya, kungiyar Azam FC ta Rwanda ce ta lashe kofin, bayan da ta samu nasara kan abokiyar karawar ta wato Gor Mahia FC ta kasar Kenya da ci 2 da nema. Sakamakon hakan kulaf din Rwanda ya samu kyautar kudi har dalar Amurka 30,000, yayin da kulaf na biyu wato kungiyar Kenya, ta karbi kyautar dalar Amurka 20,000.

Kungiyoyi 13 da suka buga wannan gasa dai sun hada da Tanzania, da Kenya, da Djibouti, da Zanzibar, da Sudan.Sai kuma Rwanda, da Burundi, da Somalia, da Sudan ta kudu, da Habasha da kuma kasar Uganda.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China