in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kocin Zambia ya bayyana kwarin gwiwar sa game da halartar gasar Olympics ta birnin Rio
2015-08-05 09:35:20 cri
Mai horas da 'yan wasan kwallon kafar kasar Zambia ajin matasa 'yan kasa da shekaru 23 Fighton Simukonda, ya bayyana kwarin gwiwar sa game da burin kungiyar sa, na samun gurbin buga gasar Olympic ta Rio de Janeiron kasar Brazil, gasar da ke tafe cikin shekarar 2016 mai zuwa.

Jaridar Daily Mail ta Zambia ta rawaito koci Simukonda na cewa nasarar da Zambia ta samu, na doke takwararta ta Cote d'Ivoire da ci 4 da 3 a bugun daga kai sai mai tsaron gida ta dada karfafa masa gwiwa.

Duk da wannan tagomashi da kocin na Zambia ke ganin kungiyar sa na samu, a hannu guda ya ce dole ya kara karfin 'yan wasan gaban sa, gabanin sauran wasannin share fage da ake bugawa domin halartar gasar cin kofin gasar kulaflikan matasan wanda za a gudanar a kasar Senegal. Kuma kulaflikan da suka samu nasara a gasar za su wakilci nahiyar Afirka zuwa gasar Olympic ta birnin Rio a badi.

Kulaflikan da tuni suka cimma nasarar samun gurbi a gasar ta Senegal dake tafe sun hada da Algeria, da Masar, da Afirka ta Kudu da kuma mai masaukin gasar Senegal.

Bisa tsari kungiyoyi uku da suka samu zama a sahun gaba a gasar ta kasar Senegal, na da gurbin halartar gasar Olympic ta Rio kai tsaye, yayin da kuma kungiya ta 4 za ta fafata neman gurbin ta hanyar karawa da wata kasa daga nahiyar Asiya.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China