in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakamakon wasannin share fage na gasar Olympic ta birnin Rio
2015-08-05 09:36:29 cri
A ci gaba da fafatawar da ake yi domin share fagen shiga gasar kwallon kafa, ta matasa 'yan kasa da shekaru 23 wadda za ta gudana a kasar Senegal, tsakanin ranekun 28 ga watan Nuwamba zuwa 12 ga watan Disamba, ga sakamakon wasannin zagaye na 2 a makwanni na 3.

A wasannin da aka buga a filin wasa dake Pointe-Noire, na kasar Congo Brazzaville

Congo 0 Nigeria 0, wanda hakan ke nuna Nigeria ta samu nasara kan Congo da tsiran maki, bayan da jimillar kwallayen wasannin da suka buga suka zamo 2-1.

A Blida na kasar Algeria kuwa, Sierra Leone 0 Algeria 0, kuma Algeria ta samu nasara ke nan da yawan kwallaye 2-0

Wasan da aka mayar birnin Bamako sakamakon barkewar cutar Ebola kuwa, Mali ta doke Gabon da ci da nema, don haka Mali ke kan gaba da yawan kwallaye 3-0.

Sai wasan birnin Lusaka, inda Zambia ta tashi wasanta da Ivory Coast babu ci bisa tazarar maki da Zambia ta samu na kwallo 4-3.

A Kampala kuwa, Masar ta doke Uganda da ci 2 da 1. Masar ta samu nasara da yawan kwallaye 6 da 1 ke nan.

Sai kuma wasan birnin Pietermaritzburg na Afirka ta tsakiya, inda Afirka ta Kudu ta samu nasara kan Zimbabwe da ci 3 da nema, kuma ta yi gaba da yawan kwallaye 4-1

A Rades na kasar Tunisia kuwa, Tunisia ta doke Morocco da ci 2 da nema. Don haka Tunisia ta shige gaba da yawan kwallaye 2 da 1.

Bisa jimillar wasannin da aka buga, kungiyoyi 7 da suka cimma nasara a wannan wasanni na share fage za su shiga gasar ta nahiyar Afirka da za a buga a kasar Senegal.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China