in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta bukaci Sudan da Sudan ta kudu da su kafa yankin kan iyaka maras makamai
2015-08-04 10:36:01 cri
Shugaban kwamitin aiwatarwa na kungiyar AU kan maganar Sudan, kuma tsohon shugaban kasar Afirka ta Kudu Thabo Mbeki, ya bukaci kasashen Sudan da Sudan ta kudu da su koma teburin shawara, domin cimma burin kafa yankin kan iyaka maras makamai na kasashen biyu.

Mr. Mbeki wanda ya jagoranci tawagar ta AU, a yayin ziyarar da suka kaiwa shugaba Omar al-Bashir na Sudan a jiya Litinin, ya shaidawa 'yan jarida cewa daya daga muhimman batutuwan da suka zanta da shugaba Al-Bashir akai shi ne batun aniyar kasashen biyu, na wanzar da tsaro a kan iyakokin su.

Ya ce don gane da hakan ne ma kwamitin sa, ke shirin kiran wani taro na masu ruwa da tsaki a fannin siyasa da tsaron kasashen biyu, da nufin tabbatar da kafuwar wannan yanki mai muhimmanci.

A daya bangaren kuma, mataimaki ga shugaban kasar Sudan Ibrahim Mahmoud Hamid, ya bayyana aniyar kasar sa na aiwatar da yarjejeniyar hadin gwiwa da kasashen biyu suka rattabawa hannu a shekarar 2012. Ya ce Sudan ta amince da tsarin kungiyar AU na kafuwar yanki maras makamai, koda yake a cewar sa, da fari Sudan ta Kudu ta amince da wancan tsari, kafin daga bisani ta sauya matsaya, lamarin da ya gurgunta burin cimma nasarar kafuwar yankin. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China