in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da sabon hari a wani caji ofis na 'yan sanda a arewacin Kamaru
2015-07-27 21:40:28 cri
Rahotanni daga kasar Kamaru na cewa wasu da ake kyautata zaton 'yan Boko Haram ne, sun kaddamar da hari kan wani sansanin rundunar 'yan sanda dake kauyen Afade a yankin arewa mai nisa dake kasar.

A cewar wani jami'in rundunar sojin kasar da ya bukaci a boye sunan sa, maharan sun tsallaka zuwa kasar Kamaru ne ta kan iyakar Najeriya da sanyin safiyar Litinin din nan, inda kuma suka aukawa sansanin na 'yan sanda. Ya ce sun kone wasu motoci guda biyu, sa'an nan sun hallaka mutane biyu da ake tsare da shi a ginin na 'yan sanda.

Kaza lika jami'in rundunar sojin ya ce bayan aukuwar lamarin, wasu sojoji 4 da 'yan sanda 3 sun yi batan dabo, ko da yake dai ba a tabbatar da ko maharan ne suka yi awon gaba da su ba.

An ce maharan sun tsare bayan farmakin da suka kaddamar, kafin jami'an tsaro su isa wurin domin daukar wani mataki.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China