in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin ta'addanci ba zai kawo illa ga dangantaka tsakanin Somaliya da Sin ba, in ji ministan harkokin wajen Somaliya
2015-08-01 14:00:08 cri
A ranar Alhamis 30 ga wata, yayin da yake magana tare da wakilin CRI a birnin Mogadishu, ministan harkokin wajen kasar Somaliya, Abdusalam H. Qmer ya nuna bakin cikinsa kan mutuwar wani jami'in ofishin jakadancin Sin dake Somaliya sakamakon harin ta'addanci da aka kai wa Otel din Al-Jazeera a kwanan baya. Amma ya ce, wannan ba zai kawo illa ga dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu ba.

Mr. Qmer ya ce, kasar Somaliya ta nuna godiya sosai ga goyon baya da jama'a da gwamnatin Sin suka ba ta. A matsayin wata babbar kasa a duniya, an sake bude ofishin jakadancin Sin a Somaliya a bara. Wannan ne muhimmin goyon baya da Sin ta baiwa jama'ar Somaliya. Kasar za ta ba da taimako wajen sake zabar wani wurin ofishin jakadancin Sin a Somaliya bisa iyakacin kokarinta, tare da daukar kwararran matakan tabbatar da tsaro a can.

Dadin dadawa, Mr. Qmer ya kara da cewa, ta'addanci ya zama babbar matsalar da kasashen duniya ke fuskanta. Gwamnatin Somaliya za ta ci gaba da hadin gwiwa da sauran kasashen duniya domin yaki da kungiyar Al-shabaab. 'Yan ta'addan suna kai hari ne ba tare da nuna bambanci ba, ba za su mai da hankali kan wadanda suka kashe Sinawa ne ko mutanen Somaliya, musulmai ne ko ba musulmai ba. Amma duk da haka, wannan ba zai yi illa ga dangantakar da ke tsakanin Somaliya da Sin ba, in ji mr. Qmer.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China