in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta cimma nasarar karbar bakuncin gasar Olympic ta shekarar 2022
2015-07-31 18:14:29 cri

A yau Jumma'a ne shugaban kwamitin gasar wasannin Olympics na duniya Thomas Bach, ya bayyana sunan birnin Beijing, a matsayin birnin da ya samu nasarar lashe zaben da aka kada, domin zabar birnin da zai karbi bakuncin gasar Olympics a yanayin sanyi ta shekarar 2022.

Mr. Thomas ya bayyana hakan ne a birnin Kuala Lumpur na kasar Maleshiya, yana mai cewa don haka birnin na Beijing ne zai kasance birni daya tak a duniya, wanda ya samu damar shirya gasar Olympics a yanayin zafi da yanayin sanyi baki daya.

A shekarar 2008 ne dai birnin Beijing ya gudanar da gasar wasannin Olympics na yanayin zafi karo na 29, tare da cimma gagarumar nasara. A wannan karo kuma, zai yi hadin gwiwa tare da birnin Zhangjiakou, wajen shirya wata babbar gasar wasannin Olympics. Bisa jimilla an kiyasta cewa, za a kashe kudi dala biliyan 1.5 wajen gudanar da wannan gasa.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China