in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar birnin Beijing ta kammala gabatar da bayanin neman karbar bakuncin gasar wasannin Olympics a lokacin sanyi na shekarar 2022
2015-07-31 15:51:51 cri
A tsakiyar ranar yau ne, tawagar birnin Beijing da ke neman daukar bakuncin gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi ta kammala gabatar wa taron kwamitin wasannin Olympics da aka yi a birnin Kuala Lumpur dake kasar Malaysia bayananta.

A yau da dare ne kuma ake saran mambobin kwamitin shirya gasar wasannin Olympics na duniya 85 za su jefa kuri'u don zaben birnin da zai karbi bakuncin wasannin Olympics na lokacin sanyi na shekarar 2022.

Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya yi jawabi ta hoton bidiyo, inda ya nuna goyon bayansa ga birnin na neman shirya gasar wasannin Olympics na lokacin sanyi. Ya ce, jama'ar Sin na fatan samun wannan dama,kuma idan har aka zabi birnin Beijing, tabbas Sin za ta shirya gasar wasannin Olympic mai kayatarwa kuma cikin nasara.

Mataimakiyar firaministan kasar Sin Madam Liu Yandong ta ce, gwamnatin Sin a shirya ta ke ta kebe isassaun kudade da matakan tsaro don shirya gasar wasannin na Olympics.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China