in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yadda kasar Sin ta kaddamar da dokar tsaron kasa wani mataki ne mai muhimmanci, a cewar tawagar kasar
2015-07-28 10:10:36 cri
Zaunanniyar tawagar kasar Sin a birnin Geneva ta sanar a ranar Litinin cewa, yadda kasar Sin ta kaddamar da dokar tsaron kasa wani muhimmin matakin ne da gwamnatin kasar ta dauka don cimma burinta na tafiyar da harkokin mulki bisa doka.

Tawagar ta bayyana cikin wata sanarwa cewa, sabuwar dokar da aka kafa za ta ba da damar gudanar da harkokin tsaron kasar Sin bisa doka. Tana ganin cewa, da farko dai, an tsara dokar ce da nufin tinkarar kalubalolin da ake fuskanta a fannin tsaro, gami da kokarin gudanar da harkokin mulki bisa doka.

Sa'an nan na biyu, tsara dokar tsaron kasa wata al'ada ce da kasashe daban daban suke bi, yayin da dokar tsaron kasar Sin ta dace da muhallin kasar, da ka'idojin kasa da kasa, haka kuma an yi koyi da nagartattun fasahohi na kasashe daban daban a kokarin tsara ta.

Abu na uku da tawagar kasar Sin ta bayyana cikin sanarwar shi ne, duk wata kasa ko kuma al'umma, tilas ne ta yi kokarin samun daidaituwa tsakanin hakkin mutane da nauyin dake bisa wuyansu. Sabili da haka, sabuwar dokar da kasar Sin ta tsara ta kayyade wasu abubuwa dangane da iko da nauyin dake bisa hukuma, gami da daidaikun mutane da kungiyoyi. Haka kuma na hudu, a cewar tawagar kasar Sin, an tsara wannan doka ce don tabbatar da kare hakkin dan Adam, ganin yadda dokar ta jaddada manufar tabbatar da tsaron jama'a, ta kuma kayyade cewa, duk wani matakin da za a dauka a fannin tsaron kasa, za a yi shi ne domin kare jama'a, sa'an nan za a dogaro kan jama'a don tabbatar da tsaron kasar.

A ranar 1 ga watan Yulin da muke ciki ne aka kaddamar da dokar tsaron kasar ta Sin.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China