in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya bukaci baiwa mata kariya yayin tashe-tashen hankula
2014-10-29 10:13:09 cri

Wakilin din din din na kasar Sin a MDD Liu Jieyi, ya bayyana bukatar baiwa mata cikakkiyar kariya a yankunan dake fama da rigingimu, tare da sanya su cikin shirin wanzar da sulhu, da ma manufofin yaki da ta'addanci.

Mr. Liu wanda ya bayyana hakan yayin zaman kwamitin tsaron MDDr ya ce, akwai bukatar kasashe duniya su yi hadin gwiwa, wajen baiwa mata irin kariyar da ta dace, duba da yadda su kan fuskantar tarin kalubale da cin zarafi iri-iri a lokutan yaki ko tashe-tashen hankula.

Wakilin kasar ta Sin ya kara da jaddada muhimmancin magance wannan matsala tun daga tushe, yana mai bayyana bukatar hadin kai wajen baiwa matan da suka tsinci kan su cikin wannan halin tallafin jin kai tare da cikakkiyar kariya ga rayukansu. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China