in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu fashewar tagwayen boma-bomai a arewacin kasar Kamaru
2015-07-23 09:45:49 cri

Wasu tagwayen boma-bomai sun tarwatse a birnin Maroua na yankin arewa mai nisa dake kasar Kamaru, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla 20, yayin da kuma wasu mutane fiye da 30 suka ji raunuka.

Wani jami'in sojan kasar ta Kamaru ya bayyanawa wakilin kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, boma-boman sun tashi ne a babbar kasuwar Maroua da karfe 2 da rabi na yammacin wannan rana, kuma kasuwar na daya daga cikin wuraren da jama'a ke taruwa a birnin na Maroua.

Ana dai zargin mayakan kungiyar Boko Haram da kaddamar da wannan hari.

A daya hannun kuma yawan mutanen da suka mutu a sakamakon fashewar boma-boman zai iya karuwa, duba da yawan mutanen da suka samu munanan raunuka a yayin aukuwar wannan lamari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China