in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rangadin ministan harkokin wajen kasar Sin a nahiyar Afrika ya karfafa dangantaka da zumunci a tsakanin bangarorin biyu
2015-01-18 16:36:09 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya kammala rangadin aikinsa a nahiyar Afrika a ranar Jumma'a, wanda ya kai shi a kasashen Kenya, Sudan, Kamaru, Guinee-Equatoriale da RDC-Congo. Wannan rangadi nada manufar karfafa huldar dangantaka ta moriyar juna tsakanin Sin da kasashen Afrika a fannonin siyasa, tattalin arziki da tsaro, in ji mista Wang a birnin Kinshasa, hedkwatar RDC-Congo. Shugaban diplomasiyyar kasar Sin ya bayyana cewa kasar Sin na bada babban muhimmanci ga sahihiyar abokantaka da take rabawa tare da kasashen Afrika, kuma tana son cigaba da aiwatar da ita cikin adalci da gaskiya wajen neman moriyar juna, da samun sakamako mai alfanu ga kowa, da cimma maradun cigaban hadin gwiwa.

A kasar Kenya, mista Wang ya shawarta cewa kasashen biyu suna hada dangantakarsu a cikin muhimman bangarori bakwai, kamar zamanintar da aikin noma, bunkasa ababen more rayuwa, makamashi mai tsabta, domin kara zurafa hulda da abokantaka tsakanin kasashen biyu.

A kasar Kamaru, mista Wang ya bayyana cewa kasar Sin zata cigaba da kyautata yardar juna ta fuskar siyasa tare da kasar Kamaru, bunkasa dangantakar moriyar juna, bisa tushen bukatun cigaba na kasar Kamaru da kuma kwarewar Sin.

A kasar Guinee Equatoriale, ministan harkokin wajen Sin ya sanar da cewa kasar Sin zata cigaba bunkasa dangantaka tare da kasar Guinee a bangaren makamashi da ma wasu bangarori.

A kasar RDC-Congo, babban jami'in diplomasiyyar kasar Sin ya bayyana cewa ya kamata Beijing da Kinshasa su cigaba da tallafawa juna ta fuskar siyasa, neman sakamako na moriyar juna a fannin tattalin arziki, da kuma zurfafa dangantaka a bangaren tsaro.

Bayan karfafa huldar siyasa da dangantakar tattalin arziki, wani muhummin bangare na ziyarar mista Wang a nahiyar Afrika shi ne na kawo goyon bayan kasar Sin ga hukumar cigaban kasa da kasa ta IGAD, wato kungiyar shiyyar dake kunshe da kasashen gabashin Afrika guda takwas, domin maido da zaman lafiya da zaman karko a Sudan ta Kudu.

Har wa yau a yayin wannan rangadi nasa, ministan harkokin wajen kasar Sin ya gana da manyan jami'an IGAD da kuma bangarorin dake gaba da juna a kasar Sudan ta Kudu a ranar 12 ga watan Janairun a Khartoum babban birnin kasar Sudan.

A yayin wannan ganawa, bangarorin dake yaki da juna a Sudan ta Kudu sun samu amincewa da juna domin gaggauta shirin wanzar da zaman lafiya a cikin kasar tare da kuma nuna godiyarsu ga kasar Sin kan taimakonta game da kokarin shiga tsakani na kungiyar IGAD. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China