in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Faransa ya bukaci Kamaru da Nigeriya da su yi aiki tare wajen yaki da kungiyar Boko Haram
2015-07-04 18:30:33 cri
Shugaban kasar Faransa Francois Hollande wanda yake ziyarar aiki a kasar Kamaru a ranar Jumma'an nan ya yi kira ga kasashen Kamarun da Nigeriya da su yi aiki tare wajen yakar kungiyar boko haram wanda yake kawo cikas ga zaman karko da kwanciyar hankali a kasashen biyu da ma makwabtansu Chadi da jamhuriyar Niger.

Mr. Hollande da yake jawabi jim kadan bayan ganawa da shugaban kasar ta Kamaru Paul Biya yace kwanan nan shugaban kasar Nigeriya zai kawo ziyarar aiki a Kamaru don haka yana da matukar muhimmanci ga kasashen biyu sun samu dangantakar zumunci mai kyau.

Shugaban na Faransa dai ya isa Kamaru ne Jumma'an nan da rana bayan da ya ziyarci kasashen Benin da Angola. Wannan ne karo na farko da wani shugaban kasar Faransa ya ziyarci Kamaru cikin shekaru 14 tun bayan da tsohon shugaban kasar na Faransa Jacques Chirac ya je lokacin babban taron Faransa da Afrika a shekara ta 2001.

Shugaban kasar Kamaru a nashi bayanin yace batun yaki da kungiyar boko haram shi ne a kan gaba a ganawar da yayi da shugaban kasar ta Faransa Francois Hollande.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China