in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Harin da Amurka ta kaddamar da jirgi maras matuki ya hallaka shugaba na biyu na kungiyar IS dake Afghanistan
2015-07-09 10:26:33 cri
Rahotanni daga kasar Afghanistan, na cewa sojin Amurka sun hallaka Gül Zaman, shugaba na biyu na kungiyar IS dake kasar Afghanistan, sakamakon wani hari da suka kaddamar da jirgin sama maras matuki a daren ranar Talata.

An ce dakarun Amurka sun yi luguden wuta ta sama a jihar Nangarhar dake gabashin kasar, lamarin da ya sabbaba kisan jagoran na IS.

Ita ma hukumar tsaron kasar Afghanistan ta bayyana cewa Gül Zaman, da sauran mambobin kungiyar IS guda shida sun rasa rayukansu a sakamakon hare-haren da jirgin sama maras matuki na kasar Amurka ya kaddamar. Ko da yake ba ta bayyana hakikanin lokacin da aka kaddamar da hare-haren ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China