in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun MDD ya bayyana bukatar kawo karshen kungiyar IS
2015-04-21 15:41:11 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa a daren ranar Litinin, inda ya yi Allah wadai da kisan wasu kiristoci 'yan kasar Habasha da reshen kungiyar IS dake kasar Libya ya yi.

Sanarwar ta kuma jaddada cewa, tilas ne a ci gaba da daukar matakan kawo karshen kungiyar IS, da kawar da tsattsauran ra'ayinta na tada hankula, tare da gurfanar da masu hannu cikin ayyukan ta'addanci a gaban kotu.

Kwamitin sulhun ya yi kira ga dukkan kasashen duniya da su bi dokokin kasa da kasa, da kudurin kwamitin sulhun game da wannan batu, da yin hadin gwiwa tare da kasashen Libya da Habasha.

Hakazalika kuma, kwamitin sulhun ya bukaci kungiyar IS, da kungiyoyin dake da nasaba da Al-Qaida, da su saki dukkan mutanen da suka yi garkuwa da su nan take ba tare da gindaya wani sharadi ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China