Ma'aikatar tsaron kasar ta ba da wata sanarwa, inda ta tabbatar da wannan labari. Ta ce, bisa rahoton sirrin da aka samu, an ce, harin da kawancen kasa da kasa dake karkashin shugabancin Amurka suka kai a wani masallacin garin TalAfar dake jihar Ninewa a yankin arewacin Iraqi, ya haddasa mutuwar mataimakin shugaban kungiyar IS Abu Ala Afri, gami da wasu masu tsattsauran ra'ayi da dama dake taro a wajen.
Shafin Internet na ma'aikatar tsaron kasar ya kuma nuna hoton biyo, inda ya nuna cewa fashewar bom ta lalata duk masallacin din.(Bako)