in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban kasar Sin ya gana da takwaransa na Zimbabwe
2015-07-08 19:39:51 cri
A yau ne mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao ya gana da takwaransa na kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa a nan birnin Beijing.

Mr Li wanda ya tabo tarihin hadin gwiwar kasashen biyu yayin jawabinsa, ya yi fatan sassan biyu za su yi mafani da bikin cika shekaru 35 da kulla huldar diflomasiya wajen daga dangantakar da ke tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi.

Ya ce, jam'iyyar kwaminis ta kasar Sin za ta kara karfafa musaya tsakaninta da jam'iyyar ZANU-PF don bunkasa ci gaban da ke tsakanin kasashen biyu.

A jawabinsa Mnangagwa wanda har ila shi ne mataimakin shugaban jam'iyyar ZANU-PF mai mulki a kasar ta Zimbabwe ya ce, kasashen biyu da kuma jam'iyyunsu za su ci gaba da karfafa hadin gwiwar da ke tsakanisu ta yadda za ta kara fadada. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China