in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Yuanchao ya zanta da mataimakin shugaban kasar Tanzania
2015-05-20 21:16:31 cri
Mataimakin shugaban kasar Sin Li Yuanchao, ya gudanar da shawarwari tare da mataimakin shugaban kasar Tanzania Mohammed Charisb Bilal, wanda ke ziyarar aiki a nan kasar Sin.

A yayin shawarwarin da suka gudanar a jiya Laraba a nan birnin Beijing, Mr. Li Yuanchao ya bayyana cewa, Sin da Tanzania abokai ne a kowane yanayi, kuma kasar Sin tana fatan ci gaba da kwazo tare da kasar Tanzania, wajen aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito a kan su.

Kaza lika Sin na da burin kara hadin gwiwa da kasar a fannonin ayyukan more rayuwa, da makamashi, da harkar sufurin jiragen sama, da gina yankin masana'antu da dai sauransu, ta yadda hakan zai taimaka, wajen inganta dangantakar abokantaka ta hadin gwiwa a tsakanin sassan biyu.

A nasa bangare, Bilal ya bayyana cewa Tanzania, na dora muhimmanci kan zumuncin dake tsakaninta da kasar Sin, kuma tana da burin koyi daga fasahohin Sin a bangaren yin kwaskwarima, da bude kofa. Tana kuma maraba da kamfanonin Sin a fannin zuba jari. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China