in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeriya ta nada Firaministan wucin gadi kafin babban zaben kasar
2014-03-14 09:24:22 cri
An nada Ministan makamashi na kasar Algeriya a matsayin sabon firaministan wucin gadi a ranar Alhamis din nan don ya maye gurbin Abdelmaek Sellal wanda ya yi murabus domin karban mukamin mai yakin neman zaben Shugaban kasar na yanzu Abdelaziz Bouteflika da za'a yi a ranar 17 ga watan Afrilu.

Sanarwar da ta fito daga ofishin shugaban kasar ta ce Shugaba Bouteflika ya kuma nada Ahmed Ouyahia a matsayin Ministan kasa kuma Shugaban ma'aikata na ofishin Shugaban kasar wanda ya maye gurbin Mohammed Moulay Guendil wanda aka ba shi wani aiki daban.

Shi kuma Abdelaziz Belkhadem aka nada shi Ministan kasa kuma mai baiwa Shugaban kasa shawara na musamman, in ji sanarwar.

Mr. Ouyahia da Mr. Belkhadem dukkanninsu tsoffin firaministoci ne kuma tsoffin shugabannin jami'iyun dake mulkin kasar wato National Democratic Rally ko (RND) da kuma Liberation Front (FLN). (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China