in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 3 ne suka mutu sakamakon girgizar kasa a jihar Xinjiang
2015-07-04 13:50:55 cri
Bisa alkaluman da hukumar sadarwa ta kwamitin jam'iyyar kwaminis ta Sin na jihar Uygur mai zaman kansa na Xinjiang ta bayar, an ce, ya zuwa yammacin ranar Jumma'a da misalin karfe 6, baki daya mutane 3 ne suka mutu yayin da wasu 71 suka jikkata sakamakon abkuwar girgizar kasa mai karfin digiri 6.5 bisa ma'aunin Richter a wannan rana da karfe 9 da minti 7 a gundumar Pishan ta yankin Hetian na jihar Xinjiang. Yanzu ana gudanar da aikin ceto yadda ya kamata. Mahukuntan wurin na kokarin daidaita batun tsugunar da jama'a da bayar da abinci da jiyya a gare su da kuma batuttuwa makamantansu.

Bayan abkuwar girgizar kasa, jihar Xinjiang ta fitar da shirin ko ta kwana a matsayi na biyu, wadda ta tura rukunin ma'aikata zuwa wurin da ake fama da bala'in, tare da kebe kudin agaji yuan miliyan 20 ga wannan yanki. Ya zuwa yanzu, an isar da tantuna sama da 1500, da barguna 2000, da tufafin masu tare sanyi 2000 da sauransu a yankin dake fama da bala'in. Har ila yau , an tura wata tawagar likitoci da ke kunshe da motocin ba da jiyya 9 da likitoci kwararru 33 daga birnin Urumqi, hedkwatar jihar, zuwa wurin, yayin da hukumar kula da bala'in girgizar kasa ta yankin Xinjiang ta tura rukunoni biyu da ke kunshe da ma'aikata 20 zuwa wurin cikin gaggawa domin gudanar da ayyukan tinkarar bala'in.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China