in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta fitar da shirin ko ta kwana game da girgizar kasa a Xinjiang
2015-07-03 17:51:21 cri
Hukumomi a kasar Sin sun fitar da shirin ko ta kwana dangane da girgizar kasa mai karfin maki 6.5 da ya auku tare da hallaka mutane 6 a garin Pishan da ke yankin Xinjiang mai cin gashin kanta na Uygur da misalign karfe 9 na safiya ranar jumma'ar nan.

Ma'aikatar harkokin harkokin cikin gida ta kasar da hukumar rage aukuwar bala'u ta kasar sun aika da jami'ai domin aikin ceto a wannan yankin, tare da yin kira da a samar da kayayyakin jin kai. Ya zuwa yanzu an riga an aika da tantuna 1,000 a wajen.

Fiye da sojoji da masu kayan sarki 500 daga sansanin Soji na Lanzhou sun riga sun isa wajen domin taimakawa wajen neman wadanda bala'in ya rutsa da su. Har ila yau jami'an kiwon lafiya 22 su ma an aika da su wannan yankin na Pishan.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China