in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yanke hukunci ga masu yin ayyukan ta'addanci a birnin Urumqi
2014-12-09 16:11:20 cri
Wata kotun birnin Urumqi dake jihar Xinjiang ta kasar Sin ta yanke hukunci ga wasu mutanen da suka aikata ayyukan ta'addanci a tashar jiragen kasa ta kudu da ke birnin Urumqi a ranar 30 ga watan Afrilu da kuma arewacin titin Gongyuan a ranar 22 ga watan Mayun bana, inda aka yankewa mutane 8 hukuncin kisa, sai mutane 5 da aka yankewa hukuncin kisa tare da daurin wasu shekaru na jeka ka gyara halinka, da kuma mutane 4 da aka yankewa hukuncin daurin rai da rai ko zaman wakafi na dan wani lokaci.

A daren ranar 30 ga watan Afrilu na bana ne, wasu mutane suka tayar da wani bam a shigar tashar jiragen kasa ta birnin Urumqi, wadda ta haddasa mutuwar mutane uku, ciki har da wani fararen hula guda daya da kuma maharan guda biyu, kana mutane 79 sun ji rauni, guda 4 a cikinsu sun ji rauni mai tsanani.

Sa'an nan a safiyar ranar 22 ga watan Mayu, wani bam ya tashi a wata kasuwa dake titin Gongyuan dake birnin Urumqi, lamarin da ya haddasa mutuwar fararen hula 39, kana wasu mutane 94 suka ji rauni.

A ranar 23 ga watan Mayu, an samu nasarar kama mutane biyar din da ake zargi da aikata laifin sai dai hudu daga cikinsu sun mutu yayin da suke kokarin tayar da bam din, koda ya ke a daren ranar 22 ga watan Mayu an kama sauran cikon na biyar din da ke tsara yadda za su wadannan hare-hare. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China