in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu zai kakaba takunkumi ga masu neman gurgunta shirin zaman lafiyar kasar Mali
2015-06-30 10:02:52 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya ce, a shirye yake ya garkama takunkumi ga duk wanda ya yi kokarin kawo cikas ga aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiya da aka cimma a kasar Mali.

A cikin kudurin da kwamitin mai mambobi 15 ya cimma, kwamitin ya kuma bukaci gwamnatin kasar Mali da kungioyin da ke dauke da makamai a cikin kasar da su cika alkawuran da suka dauka kana su mutunta yarjejeniyar tsagaita bude wutar da suka cimma.

Kwamitin sulhun ya kuma dorawa tawagar MINUSMA da aka kafa a shekarar 2013 dake kasar ta Mali alhakin taimakawa shirin kasar na mayar da mulki ga hannun farar hula, da sa-idon ganin an aiwatar da yarjejeniyoyin tsagaita bude wuta da kuma na zaman lafiya da aka cimma a kasar.

Tun a watan Afrilu ne fada ya sake barkewa a arewacin kasar Mali tsakanin Buzaye 'yan tawaye da mayakan da ke goyon bayan gwamnati. MDD dai na kira ga bangarorin da ke fada da juna a kasar Mali da su kawo karshen matsalar da kasar ke fuskanta ta hanyar aiwatar da yarjejeniyar zaman lafiyar da aka cimma. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China