in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sanar da sabon lokacin gudanar da babban zaben kasar Burundi
2015-06-11 10:34:59 cri
A jiya Laraba 10 ga watan nan ne shugaban kasar Burundi Pierre Nkurunziza, ya bayyana ranar 29 ga watan nan, a matsayin ranar da za kada kuri'u a zaben majalisar dokokin kasar sa, yayin da kuma zaben shugaban kasar zai biyo baya a ranar 15 ga watan Yuli, kana a gudanar da zaben majalisar dattijan kasar a ranar 24 ga watan na Yuli.

Bisa tsarin mulkin kasar ta Burundi, al'ummar kasar na zabar shugaban kasar, wanda ke jagorantar kasar a tsahon wa'adin shekaru 5, kana shugaba mai ci na iya kasancewa kan karagar mulkin kasar a karo biyu.

Majalissar dokokin kasar Burundi ce dai ta amince da shugaba Nkurunziza ya jagoranci kasar Burundi a shekarar 2005. Kana ya sake samun damar zarcewa bayan lashe babban zaben kasar na shekarar 2010. A kuma ranar 25 ga watan Afrilun da ya gabata, jam'iyyar sa ta FDD ta sake bayyana Nkurunziza a matsayin dan takarar ta a karo na uku, matakin da jam'iyyar adawar kasar ta ce ya sabawa doka.

Sai dai duk da kasancewar Nkurunziza ya jagoranci Burundi har karo biyu, magoya bayan sa na ganin shugaban na da ikon sake tsayawa takara a wannan karo, duba da cewa ya hau karagar mulkin kasar a shekarar 2005 ne ta hanyar amincewar majalissar dokoki, ba wai ta hanyar kada kuri'un al'ummar kasar ba. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China