in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burundi ta yi maraba da shawarar EAC game da dage zabe
2015-06-01 10:35:54 cri
Gwamnatin Burundi ta yi maraba da sakamakon taron kolin shugabannin kungiyar raya yankin gabashin Afirka ta EAC, taron da ya yi kira ga mahukuntan kasar da su dage zaben majalissun dokoki da na shugaban kasa, wanda a baya aka shirya gudanarwa a ranekun 5 da 26 ga watan nan na Yuni.

Kakakin gwamnatin Burundi Philipe Nzobonaliba, ya ce, dage zaben da wata guda da rabi kamar yadda EAC ta ba da shawara, zai baiwa 'yan adawa dake korafin karancin lokaci damar sake shiri na shiga zaben.

A jiya Lahadi ne dai shugabannin kasashe manbobin kungiyar ta EAC suka gudanar da taron gaggawa a birnin Dar es Salaam na kasar Tanzaniya.

Sanarwar bayan taron dai ta nuna matukar damuwar shugabannin kasashe mambobin kungiyar, game da halin kunci da ake ciki a kasar Burundi, suna masu kira da a dage zabubbukan kasar da tsawon wata guda da rabi.

Haka kuma, sanarwa ta yi kira ga bangarorin daban-daban dake kasar ta Burundi da su kai zuciya nesa, su kuma kauracewa tada hargitsi.

Shugaba Nkurunziza bai halarci taron na EAC ba, sai dai rahotanni sun ce, ya tura tawagar ministocin sa a matsayin wakilan kasar sa. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China