in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da Amurka za su taimakawa kasashen Afirka wajen gina cibiyoyin rigakafi da yaki da cututtuka
2015-06-25 13:40:14 cri
Shugaban sashen kula da harkokin hadin gwiwar kasa da kasa na kwamitin kiwon lafiya da kayyade iyali na kasar Sin Ren Minghui, ya bayyana cewa, Sin da Amurka za su yi amfani da fifikonsu domin taimakawa kasashen Afirka wajen gina cibiyoyin rigakafi da yaki da cututtuka.

Ren Minghui ya bayyana hakan ne a birnin Washington na kasar Amurka a jiya Laraba, yayin gun taron manema labaru a wani bangare na shawarwari da ake gudanarwa game da al'adu a tsakanin Sin da Amurka zagaye na shida. Ya ce kungiyar hadin kan Afirka ta AU ta amince da kara sa ido ga barkewar cututtuka a yankin, musamman a gabar da ake fuskantar yaduwar cutar Ebola.

Tun daga karshen shekarar bara kuma, kungiyar AU da gwamnatin kasar Sin, tare da gwamnatin kasar Amurka, da kuma cibiyoyin yaki da cututtuka na kasashen biyu, sun yi shawarwari kan yadda za a tsara wani shirin rigakafi da yaki da cututtuka a nahiyar Afirka.

Ren ya kara da cewa kungiyar AU, ta tura tawagar musamman domin bincikar cibiyar rigakafi da yaki da cututtuka ta kasar Sin, da tsarin sa ido ga faruwar cututttuka na kasar ta Sin. Haka zalika kuma, AU ta daddale takardar fahimtar juna kan kafa cibiyar rigakafi, da yaki da cututtuka a nahiyar Afirka, tare da cibiyar rigakafi da yaki da cututtuka ta kasar Amurka.

Yanzu haka bangarorin uku suna tattaunawa game da yadda za a dada goyon baya ga tsarin gina irin wannan cibiya a nahiyar Afirka bisa shiri na bai daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China