in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi Allah wadai da farmakin da aka kai wa hedkwatar kasar Chadi
2015-06-16 09:15:04 cri

Babban sakataren MDD Ban Ki-Moon ya bayar da sanarwa ta bakin kakakinsa a jiya Litinin, inda ya yi Allah wadai da farmakin boma-bomai da aka kai a Ndjamena, babban birnin kasar Chadi, tare da aika sakon ta'aziyya ga gwamnatin kasar da kuma jama'arta.

Sanarwar ta ce, Ban Ki-Moon ya yaba a kan rawar da kasar Chadi ta taka wajen yaki da kungiyar mai tsattsauran ra'ayi ta Boko Haram. Ya kuma jaddada cewa, ya kamata kasashen yammaci da kuma tsakiyar Afrika su karfafa hadin gwiwarsu da kafa hadaddiyar rundunar soja wajen yaki da kungiyar Boko Haram.

Kazalika, Ban Ki-Moon ya nanata cewa, ya kamata kasashe daban daban su bi dokokin jin kai da na hakkin dan Adam da kuma na 'yan gudun hijira na duniya a yayin da suke yaki da kungiyar.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China