in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya gabatar da ra'ayoyi uku game da yadda za a bunkasa yankunan teku ba tare da wata tangarda ba
2015-06-13 13:33:09 cri
Tun daga ran 8 zuwa ran 12 ga wata, an shirya taro karo na 25 na kasashe wadanda suka kulla "yarjejeniya game da dokar teku ta M.D.D." a hedkwatar majalisar dinkin duniya dake birnin New York. A yayin taron da aka yi a ranar 12 ga wata, jakada Wang Min na kungiyar kasar Sin ya gabatar da ra'ayoyi uku a madadin bangaren Sin kan yadda za a iya bunkasa yankunan teku ba tare da wata tangarda ba.

Wang Min ya nuna cewa, da farko dai, ya kamata kasashen duniya su kafa tunanin kasancewarsu tamkar cikin kungiya daya ta cimma buri daya na bunkasa yankunan teku tare, da yakar kalubale cikin hadin gwiwa, da su bada karin hadin gwiwa irin na a zo a gani domin cimma burin samun ci gaba tare. Sannan su kara yin hadin gwiwa wajen daidaita al'amura, ta yadda za a iya cimma burin bunkasa tattalin arziki da zaman al'umma da kiyaye ingancin muhalli tare. Bugu da kari, ya kamata a kara karfin kasashe masu tasowa, ta yadda za a iya tabbatar da ganin dukkan kasashen duniya sun samu ikon kafa ajanda da ka'idoji na kasa da kasa cikin zaman daidai wa daida. Ya kamata kasashen duniya su fi mai da hankali wajen daidaita matsalar yadda za a iya kara karfin kasashe masu tasowa da kuma tabbatar da ganin sun samu daidaitaccen iko a yankunan teku.

Wang Min ya kara da cewa, bangaren Sin na fatan kara yin hadin gwiwa da sauran kasashen duniya domin ba da karin gudummawa ga kokarin bunkasa yankunan teku. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China