in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhun M.D.D. ya yi Allah wadai da harin da ya hallaka jagoran jam'iyyar adawa a Burundi
2015-05-25 10:28:31 cri

Kwamitin sulhun M.D.D. ya fidda wata sanarwa, wadda ke Allah-wadai da harin da aka kai wa jagoran jam'iyyar adawa ta UDP-Zedi Feruzi, lamarin da kuma ya haddasa rasuwarsa.

Kwamitin sulhu na M.D.D. ya ba da wannan sanawa ne a jiya Lahadi, yana mai janjantawa dangin mamacin, tare da fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata sakamakon aukuwar harin. Kaza lika kwamitin ya bukaci gwamnatin Burundi da ta gurfanar da wadanda suke da hannu cikin kisan Feruzi gaban kuliya.

Har wa yau sanarwa ta ce kwamitin sulhun M.D.Dr ya yi kira a bangarorin da rikicin siyasar kasar Burundi ya shafa da su kai zuciya nisa, a sa'i daya kuma, ya bukaci gwamnati da ta dauki kwararan matakai na hana aukuwar tashe-tashen hankula a kasar.

A daren ranar 23 ga watan nan ne dai wani mahari ya harbe Zedi Feruzi har lahira, kana wani mai tsaron lafiyarsa shi ma ya rasa ransa a harin, baya ga wasu mutanen da suka jikkata kuma maharin ya tsere.

Feruzi jigo ne daga 'yan adawa da manufar shugaba Pierre Nkurunziza, ta tsayawa takara a karo na uku, tun kuma daga ranar 26 ga watan Afrilun da ya shude ake ci gaba da zanga-zangar kin jinin gwamnatin a kasar ta Burundi, lamarin da ya hallaka mutane sama da 25. (Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China