in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya yi kira da a karfafa hadin gwiwa kan hana tafiye tafiyen masu ta'addanci tsakanin kasa da kasa
2015-05-30 16:39:24 cri
Zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Liu Jieyi ya bayyana a ran 29 ga wata cewa, ya kamata a karfafa hadin gwiwar kasa da kasa domin hana tafiye tafiyen masu ta'addanci tsakanin kasa da kasa, kuma ya kamata a fuskanci wannan matsalar ta hanyoyin yin musayar bayanai da abin ya shafa, yin hadin gwiwa kan gudanarwar dokokin dake shafar harkokin yankin iyakoki da kuma yin hadin gwiwa kan aikin sa ido kan sha'anin kudi.

A wannan rana, kwamitin sulhu na MDD ya kira wani taro domin tattaunawa kan yaki da dakarun kungiyoyin ta'addanci da suka fito daga kasashen ketare. A yayin da yake jawabi, Liu Jieyi ya ce, ya kamata gamayyar kasa da kasa ta dauki matakai yadda ya kamata domin hana yaduwar bidiyoyi da kuma ra'ayoyin 'yan ta'adda ta hanyoyin zamani, da kuma lalata shirinsu na shigar da mambobi, neman kudade da kuma shirya aikace-aikaken ta'addanci.

Kaza lika, ya kamata gwamnatocin kasa da kasa su gudanar da kudurorin babban taro da kwamitin tsaron MDD da abin ya shafa yadda ya kamata, domin karfafa aikin sa ido kan harkokin intanet.

Bugu da kari, ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da gudanar da kudurin kwamitin sulhu na MDD yadda ya kamata, da kuma karfafa aikin yaki da ta'addanci bisa dokokin da abin ya shafa. A sa'i daya kuma, kasar Sin za ta ci gaba da inganta hadin gwiwar yaki da ta'addanci dake tsakanin kasa da kasa da shiyya-shiyya, da kuma samar wa kasashe masu tasowa kayayyakin yaki da ta'addanci da kuma ba su horaswa kan aikin yadda ya kamata. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China