in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-moon ya kalubalanci bangarori daban daban na Burundi da su ci gaba da yin shawarwari domin cimma matsaya guda
2015-05-23 16:30:53 cri
A jiya Jumma'a 22 ga wata, babban sakataren MDD Ban Ki-moon ya ba da sanarwar yin marhabin da gudanar da shawarwarin siyasa tsakanin bangarori daban daban na Burundi a birnin Bujumbura, hedkwatar kasar, tare da kalubalantar bangarorin da su ci gaba da yin shawarwari domin cimma matsaya a dukkan fannoni.

Sanarwar ta ce, wakilan fararen hula, da na gwamnatin kasar, da na jam'iyyu daban daban, da na kungiyoyin addinai sun halarci wannan taro, tare da wakilai daga MDD da kungiyar AU da ta EAC da dai sauransu. Ban Ki-moon ya nuna yabo ga ci gaban da aka samu bisa shawarwarin, kuma ya nanata cewa, MDD za ta ci gaba da nuna goyon bayanta ga Burundi da ma yankin.

Bisa alkaluman da hukumar 'yan gudun hijira ta MDD (UNHCR) ta bayar, an ce, daga watan Afrilun bana zuwa yanzu, baki daya kimanin mutanen Burundi dubu 100 sun yi gudun hijira zuwa Rwanda, Tanzania, Kongo Kinshasa da sauran kasashe makwabta. A jiya hukumar UNHCR ta yi kira da a kara ba da taimakon jin kai ga wadannan 'yan gudun hijira na Burundi. Dadin dadawa, a wannan rana, babban jami'in hukumar UNHCR, Antonio Guterres ya ba da sanarwar nuna bakin cikinsa ganin halin da 'yan gudun hijira suke ciki, kuma ya nuna godiyarsa ga wadannan kasashe makwabtan Burundi da su tsugunar da su yadda ya kamata. Ya yi kira ga kasashen duniya da su nuna goyon baya ga shirin ba da agajin jin kai yadda ya kamata.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China