in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Burundi ta musanta rarrabuwar kan sojojin ta bayan nadin sabon ministan tsaro
2015-05-20 20:42:42 cri
Kakakin sojin kasar Burundi Kanar Gaspard Baratuza a ranar Talata ya musanta zancen da ake yi cewa kan sojin ya rabu inda kafofin watsa labarai suka bada rahoton cewa an hana sabon ministan tsaro kama aiki.

Kanar Baratuza kamar yadda yayi bayani a cikin wata sanarwar da ya fitar yace babu wani abu kamar haka da ya faru kuma kan su a hade yake. Abin da mutane suke ji jita jita ne kawai.

Yace ana ta jita jita a cikin babban birnin Bujumbura cewa wai wassu sojoji sun ki amincewa da korar tsohon ministan tsaron Manjo Janar Pontien Gaciyubwenge.

A ranar litinin, Emmanuel Ntahomvukiye wanda bai taba samun horon soji ba, an nada shi ministan tsaron kasar, 'yan kwanaki kadan bayan wani yunkurin juyin mulki da yaci tura akan shugaban kasar Pierre Nkurunziza wanda yake takarar shugabanci a karo na uku a zaben da za a yi a watan gobe. (Fatimah)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China