in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ba za ta yi watsi da sirrikan ta ba inji shugaba Rouhani
2015-05-22 09:57:43 cri
Shugaban kasar Iran Hassan Rouhani, ya ce kasar ba za ta yi watsi da sirrikan ta da suka jibanci fannonin aikin soja da kimiyya ba, musamman wadanda suka shafi tsaron kasar, duk da cewa tana kokarin neman daddale muhimmiyar yarjejeniya don gane da batun nukiliyar ta.

Tashar gidan telabijin ta kasar Iran wato "Press TV" ta labarta cewa, shugaba Rouhani ya yi wannan tsokaci ne a Tabriz dake arewa maso yammacin kasar, yana mai cewa gwamnatinsa za ta bi umarnin da shugaban majalisar kolin kasar Ayatollah Khamenei ya gabatar a ranar Laraba, cewa ba za su amince da wata yarjejeniya, da za ta yarjewa kasashen waje samun sirrin Iran a fannonin kimiyya da aikin soja ba.

A cewar Rouhani, gwamnatin kasar za ta bi umarnin Khamenei sau da kafa, yayin da tawagar kasar mai halartar shawarwarin da ake gudanarwa za ta tsaya kan matsayinta na cewa ko kadan, ba za ta yi rangwame a wannan fanni ba.

Kafin hakan, tawagar Iran ta riga ta bayyana matsayinta na bukatar soke takunkumin da aka sanya wa kasar, da neman amincewa kasar Iran ci gaba da nazarin fasahar nukiliya, da aikin tace sinadarin Uranium. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China