in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IAEA: Ana samun ci gaba a yunkurin da ake yi na warware matsalar nukiliyar Iran
2015-05-16 15:55:11 cri
Wakilin Sin a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA Cheng Jingye, ya ce ana samun ci gaba a yunkurin da ake yi na warware matsalar nukiliyar Iran, duk da cewa akwai sauran batutuwa masu muhummanci da ake da bukatar warwarewa.

Mr. Cheng ya ce bisa tsarin da ake kai, sakamakon zaman da masu ruwa da tsaki suka yi a kasar Switzerland cikin watan Afirilun da ya gabata, yanzu haka ana maida hankali ga cimma yarjejeniyar karshe, kafin wa'adin da aka gindaya, wato nan da karshen watan nan na Yuni.

A cewarsa muhimman batutuwan da ake fatan warwarewa dai sun hada da dage takunkumin da aka kakabawa kasar ta Iran.

A daya hannun kuma, mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi, ya shaidawa kamfanin dillancin labaru na APA cewa, kasarsa na fatan cimma matsaya, wadda za ta marbata 'yancin ta, tare da dage takunkumin da aka sanya mata.

Kafin hakan dai Mr. Araqchi ya zanta da shugaban hukumar kula da makamashin Nukiya ta MDD Yukiya Amano, wanda ya dade yana bukatar Iran din ta yi bayani filla-filla, game da shirinta na mallakar makaman nukiliya, ko da yake Iran din ta kafe cewa ba ta da manufar mallakar makaman na Nukiliya. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China