in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta tura ma'aikatan wanzar da zaman lafiya 245 kasar Mali
2014-01-15 20:53:40 cri

A ranar Laraba ne rukuni na biyu mai kunshe da jami'ai da kuma sojojin kasar Sin 245 ya tashi daga birnin Harbin da ke arewa maso gabashin kasar Sin don gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya a kasar Mali.

Kwamandan tawagar Zhang Geqiang ya bayyana cewa, ma'aikatan da za su yi aikin wanzar da zaman lafiya za su kashe tsawon watanni 8 a kasar ta Mali, inda za su bayar da gudummawa ga aikin shimfida zaman lafiya a kasar da kuma sake farfado da tattalin arzikin kasar.

Baya ga wannan tawaga, kasar ta Sin ta kuma tura dakarun kiyaye zaman lafiya zuwa kasahen Liberia, Sudan, Jamhuriyar demokiradiyar Congo, Sudan ta Kudu da Lebanon.

Idan ba a manta ba, a watan Disamba ma, kasar Sin ta tura rukuni na farko na ma'aikatan kiyaye zaman lafiya, wanda ya kunshi sojoji, masu aikin gadi da ma'aikatan lafiya zuwa kasar ta Mali. (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China