in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin da shugabar kasar Brazil sun gana da manema labaru tare
2015-05-20 09:13:11 cri

Firaministan kasar Sin Li Keqiang da shugabar kasar Brazil Dilma Rousseff sun gana da manema labaru tare bayan da suka yi shawarwari a jiya Talata da safe a birnin Brasilia.

A jawabinsa Li Keqiang ya nanata cewa, a yayin da ake fuskantar matsin lamba sosai a fannin farfado da tattalin arzikin duniya, a matsayinsu na muhimman kasashe da tattalin arzikinsu ke samun ci gaba cikin sauri, kara hadin gwiwa a tsakanin kasashen Sin da Brazil zai karfafa gwiwar kasashe masu tasowa, kuma zai ba da gundummawa ga yunkurin da ake na farfado da tattalin arzikin duniya.

A nata bangare, Dilma Rousseff ta ce, kasashen Brazil da Sin za su ci gaba da yin hadin gwiwa a MDD da kungiyar G20 da kungiyar kasashen BRICS, domin kara taka rawa kan harkokin kasa da kasa da na yankuna daban daban na duniya.(Lami)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China