in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta ci gaba da ba da gudummawa ga ci gaban duniya
2013-11-02 16:42:35 cri
Mahukuntan kasar Sin sun bayyana burin kasar na ci gaba da ba da dukkanin gudummawa ga ci-gaban kasashen duniya, musamman ta hanyar hadin gwiwa da ragowar kasashen dake da burin bunkasa yanayin zaman lafiya da tsaro, da ci-gaba mai dorewa.

Firayim minstan kasar Sin Li Keqiang ne ya bayyana wannan buri na kasar ta Sin a jiya ranar Jumma'a 1 ga watan nan na Nuwamba a yayin bikin bude taron masu ruwa da tsaki kan bunkasa ci-gaban duniya, da samar da jagoranci na gari da aka fara a nan birnin Beijing, hedkwatar kasar Sin.

Li ya ce, a wannan lokaci da Sin ke kokarin warware matsalolin tattalin arziki da na zamantakewar al'umma, a hannu guda mahukuntan na sa kaimi ga samar da sauye-sauye masu ma'ana, tare da bude kofofin yin hadin gwiwa da ragowar kasahen duniya. Hakan a cewarsa, zai haifar da kyakkyawan yanayin bunkasuwa, da cimma moriyar juna a matakan shiyya-shiyya da na kasa da kasa.

Firayim minstan kasar ta Sin ya kara da cewa, wajibi ne a dauki managartan matakan samar da daidaito, da bunkasa zaman lafiya a cikin gida, muddin ana fatan samarwa al'ummar kasar sama da miliyan dubu guda kyakkyawar rayuwa a zamanance. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China