in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Sin da Indiya sun bayyana aniyar inganta dangantaka a tsakaninsu
2014-09-19 21:13:42 cri
A yau Jumma'a ne kasashen Sin da Indiya suka lashi takwabin kara inganta dangantakar kut da kut a tsakanisnu, ta hanyar yin hadin gwiwar a fannonin zuba jari,yaki da ta'addanci,aikin soja da kuma musayar al'adu.

Kasashen biyu sun bayyana abubuwan da suke son cimmawa ne cikin sanarwar hadin gwiwar da aka bayar a ranar karshe ta ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kai kasar ta Indiya.

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, sassan za su ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a kan iyakokinsu tare da warware sauran batutuwan da ke kan teburi, kafin a kai ga warware batun kan iyakokinsu.

Kasar ta indiya dai ita ce zangon karshe na ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kai kasashe 4 na tsakiya da kudancin Asiya, ziyarar da ta kai shugaba Xi kasashen Sri Lanka, da Maldives da kuma Tajikistan inda ya halarci taron hadin gwiwa na kungiyar Shanghai.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China