A yayin ganawar, Mr. Zhang Ping ya mika gaisuwar shugabannin kasar Sin tare da bayyana cewa, hadin gwiwar kasashen Sin da Malawi na fuskantar sabon zarafi, abin da ya sa kasar Sin ta sa kaimi ga kamfanonin kasar wajen zuba jari a kasar Malawi, kuma tana son ba da taimako bisa iyakarta domin bunkasa kasashen biyu tare da kawo moriyar jama'arsu gaba daya.
Ya ce majalisar wakilan jama'ar kasar Sin tana son kara tuntubar majalisar wakilan kasar Malawi domin ba da gundumawa ga bunkasuwar huldar kasashen biyu.(Lami)