Wannan makaranta wadda ake kira Chinese Bilingual College na daya daga cikin wuraren dake koyar da harshen Sinanci a Najeriya, kuma makarantar koyar da Sinanci ce ta farko a arewacin Najeriya. Gwamnatin jihar Kano ta kafa ta ne tare da taimakon gwamnatin kasar Sin, wadda ta tura malamai Sinawa guda biyu makarantar domin koyar da daliban Najeriya harshen sinanci.(Murtala)