in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin babban sakataren MDD ya yabawa kasar Sin bisa tsaida kudurin kafa kungiyoyin al'umma don shiga shirin yaki da cutar AIDS
2015-05-06 09:48:17 cri
Mataimakin babban sakataren MDD kuma direktan gudanarwa na shirin yaki da cutar AIDS na MDD majalisar Michel Sidibe ya bayyana a jiya Talata a nan birnin Beijing cewa, a madadin shirin yaki da cutar AIDS na MDD ya yabawa gwamnatin kasar Sin bisa kudurinta na kafa kungiyoyin al'umma don shiga cikin shirin yaki da cutar AIDS.

Sidibe ya bayyanawa 'yan jarida cewa, shugabannin kasar Sin sun dora muhimmanci tare da shiga ayyukan yaki da cutar AIDS, wadda wanda hakan ya taka muhimmiyar rawa wajen sa kaimi ga dukkan al'ummar kasar shiga aikin yaki da cutar. Sin ta samu nasarori kan magance da yaki da cutar AIDS, Sidibe ya ce, yana fatan Sin za ta more fasahohinta na yaki da cututtuka masu yaduwa tare da kasa da kasa.

A nasa jawabin Direktan gudanarwa na asusun yaki da cutar AIDS, tarin fuka da kuma zazzabin cizon sauro Mark Dybul ya bayyanawa 'yan jarida cewa, a cikin shekaru fiye da 10 da suka gabata, asusunsa da kasar Sin sun yi hadin gwiwa kan magance da yaki da cutar AIDS, tarin fuka da kuma zazzabin cizon sauro. Ana fatan a nan gaba, asusun zai ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasar Sin a fannin yaki da cututtuka masu yaduwa, da cin gajiyar musayar fasahohi don amfanawa al'ummomin kasashen duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China